RFI Hausa's Avatar

RFI Hausa

@ha.rfi.fr

🌍 Sashen Hausa na RFI na maraba da ku a shafin Bluesky 💻 rfi.fr/ha/ 🎧 rfi.my/kai-tsaye 𝕏 rfi.my/Xha 📷 rfi.my/IGha 🗨️ rfi.my/WAha

50 Followers  |  6 Following  |  4,668 Posts  |  Joined: 03.01.2025  |  1.7613

Latest posts by ha.rfi.fr on Bluesky

Preview
Wani harin ƴan bindiga ya yi sanadin rayukan mutum 20 a Burkina Faso Wani hari da ƴan bindiga suka kai a garin Titao na arewacin Burkina Faso, ya yi sanadin rayukan mutane aƙalla 20 a ƙarshen mako.

Wani harin ƴan bindiga ya yi sanadin rayukan mutum 20 a Burkina Faso

16.02.2026 11:08 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Wasannin da aka buga a ƙarshen mako a Premier League da Laligar Sifaniya Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta samu nasarar kaiwa zagaye na biyar na kofin F.A bayan ta doke Wigan Athletic da ci 4 da nema a wasan da suka buga ranar Lahadi.

Wasannin da aka buga a ƙarshen mako a Premier League da Laligar Sifaniya

16.02.2026 10:41 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Tawagar Iran da Amurka sun isa Geneva a ƙoƙarin shawo kan rikicinsu Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya isa birnin Geneva tare da tawagar ƙasar don halartar zagaye na biyu na tattaunawar da za ta gudana tsakaninsu da Amurka a ƙoƙarin rage tankiyar da ke tsakanin ƙasashen biyu, a wani yanayi da jagoran addini Ayatollahi Ali Khamenei ke gargaɗin tankiyar ta iya juyewa zuwa rikicin yanki.

Tawagar Iran da Amurka sun isa Geneva a ƙoƙarin shawo kan rikicinsu

16.02.2026 10:27 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Guguwar Gezani ta kashe mutum 4 a Mozambique bayan mummunar ɓarna a Madagascar Guguwar Gezani ta afkawa yankin kudancin Mozambique, kuma tuni ta kashe aƙalla mutane 4 a cewar mahukuntan ƙasar, bayan mummunar illar da ta yi a maƙwabciyarta Madagascar.

Guguwar Gezani ta kashe mutum 4 a Mozambique bayan mummunar ɓarna a Madagascar

16.02.2026 09:33 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Yajin aikin ma'aikatan filin jirgin saman Kenya ya kassara zirga-zirga a ƙasar Yajin aikin da ma’aikatan filayen jiragen saman Kenya suka tsunduma a yau Litinin ya haddasa soke tashin jirage masu yawa yayinda wasu da dama suka yi jinkirin tashi akan lokaci.

Yajin aikin ma'aikatan filin jirgin saman Kenya ya kassara zirga-zirga a ƙasar

16.02.2026 09:33 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Sojin Najeriya sun musanta cewa Amurka ta fara jibge dakaru a Kaduna da Borno Wasu manyan Sojojin Najeriya sun ƙaryata rahotannin da ke cewa Amurka ta fara jibge dakaru a wasu sassan jihohin Borno da Kaduna, domin taimakawa dakarun ƙasar wajen yaƙi da ƴan ta’adda.

Sojin Najeriya sun musanta cewa Amurka ta fara jibge dakaru a Kaduna da Borno

16.02.2026 08:40 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Najeriya: Ƴan bindiga sun yiwa mutane kusan 30 yankan rago a Neja Ƴan bindiga a jihar Neja sun sake kai mummunan hari a wasu ƙauyuka da ke cikin Ƙaramar Hukumar Borgu, inda suka kashe kusan mutane 30 ta hanyar yankan rago, tare da sace mutane da dama da kuma ƙona gidaje da shaguna.

Najeriya: Ƴan bindiga sun yiwa mutane kusan 30 yankan rago a Neja

16.02.2026 08:13 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
AU ta ce baza ta sake lamuntar juyin mulki a ƙasashen Afrika ba Shugabannin ƙasashen Afrika sun kammala taron ƙungiyarsu karo na 39 a birnin Addis Ababa na ƙasar Habasha, inda suka tattauna game da matsalolin da Nahiyar ke fuskanta.

AU ta ce baza ta sake lamuntar juyin mulki a ƙasashen Afrika ba

16.02.2026 07:19 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Ghana na neman MDD ta ayyana cinikin bayi a matsayin cin zarafin Ɗan Adam mafi muni Gwamnatin Ghana ta sanar da shirin gabatarwa da Majalisar Ɗinkin Duniya wani ƙuduri da ke buƙatar a ayyana cinikin bayi a matsayin cin zarafin Ɗan Adam mafi muni da ya taɓa faruwa a tarihin duniya.

Ghana na neman MDD ta ayyana cinikin bayi a matsayin cin zarafin Ɗan Adam mafi muni

15.02.2026 18:03 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Haduran hanya sun laƙume rayukan mutum 164 a Cote d'Ivoire Gwamnatin Ivory Coast ta yi shelar ayyana dokar ba sani ba sabo sakamakon yawaitar haduran hanya.

Haduran hanya sun laƙume rayukan mutum 164 a Cote d'Ivoire

15.02.2026 17:22 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Cutar choléra ta ɓarke a gidan yari mafi girma da ke Kinshasa Cutar mai da gudawa ko Cholera na cigaba da yaɗuwa a gidan yarin Makala mafi girma da ke  jamhuriya Dimukradiyyar Congo

Cutar choléra ta ɓarke a gidan yari mafi girma da ke Kinshasa

15.02.2026 16:28 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Shugaba Tiani ya buɗe kofar mikawa Orano na Faransa kason Uranium da ya haƙa Shugaban mulkin sojin Jamhuriyar Nijar, Janar Abourahamane Tiani, ya buɗe ƙofar mayar wa Faransa wani ɓangare na uranium da Orano ya samar, a wani mataki da ake ganin zai kawo ƙarshen ko warware taƙaddamar da aka kwashe watanni da dama ana yi tsakanin mahukunta a Yamai da kamfanin haƙar ma'adinai na Faransa kan uranium da aka haka Somaïr da ke Arlit, na arewacin ƙasar gabin juyin mulki.

Shugaba Tiani ya buɗe kofar mikawa Orano na Faransa kason Uranium da ya haƙa

15.02.2026 14:14 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Putin ba komai ba ne face fursunan yaƙi da ke azabtar da jama'a- Zelensky Shugaba Volodymyr Zelensky na Ukraine ya bayyana takwaransa na Rasha Vladimir Putin a matsayin fursunan yaƙi tare da iƙirarin cewa ba shi da isasshen lokaci a nan gaba, yayinda ya koka cewa a yanzu haka Moscow ta lalata duk wata cibiyar lantarki mai ƙarfi da ke ƙasar shi wanda ya jefa ɗimbin jama'a a matsanancin hali sakamakon sanyin da ake fama da shi.

Putin ba komai ba ne face fursunan yaƙi da ke azabtar da jama'a- Zelensky

15.02.2026 09:17 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
CFA miliyan 300 aka kashe kan harin birnin Niamey na watan jiya- Tchiani Shugaban Gwamnatin Sojin Jamhuriyyar Nijar Abderrahman Tchiani ya yi iƙirarin cewa an kashe kuɗin da ya kai CFA miliyan 300 wajen shirya harin filin jirgin saman birnin Niamey yana mai nanata zargin da ya yi tun da farko na cewa shugaba Emmanuel Macron na Faransa da Patrice Talon na Benin da kuma Alassane Ouattara na Cote d’Ivoire ne ke da hannu a harin.

CFA miliyan 300 aka kashe kan harin birnin Niamey na watan jiya- Tchiani

15.02.2026 09:03 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Ana zaman ɗar-ɗar a Kwara bayan harin da ya kashe mutane 46 a jihar Ana ci gaba da zaman ɗarɗar a jihar Kwara ta tsakiyar Najeriya bayan harin ƴan ta’addan da ya kashe mutane aƙalla 46 galibinsu sakamakon harbin bindiga ko kuma yankan rago da ɓatagarin suka riƙa yi musu.

Ana zaman ɗar-ɗar a Kwara bayan harin da ya kashe mutane 46 a jihar

15.02.2026 08:50 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Karo na biyu a makwanni 2 gobara ta sake yin ɓarna a kasuwar singa da ke Kano Karo na biyu a jere cikin ƙasa da makwanni biyu, kasuwar sayar da kayakin masarufi ta Singa da ke jihar Kano a arewacin Najeriya ta sake gamuwa da ibtila’in gobara a yammacin jiya Asabar bayan da wuta ta sake tashi da misalin ƙarfe 4 na yammaci tare da ɓarnata dukiya mai tarin yawa.

Karo na biyu a makwanni 2 gobara ta sake yin ɓarna a kasuwar singa da ke Kano

15.02.2026 08:38 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Mutane dubu 200 sun yi gangamin goyon bayan ɗan Basaraken Iran na ƙarshe Fiye da mutane dubu 200 ne suka gudanar da wani gangami a birnin Munich na Jamus jiya Asabar don mara baya ga ɗan Basaraken Iran ko kuma "shah" na ƙarshe wato Reza Pahlavi da nufin nuna adawa da gwamnatin juyin juya halin Iran wadda yanzu haka ke tsaka da takun saƙa da Amurka kuma ake fargabar ɓarkewar yaƙi a tsakaninsu.

Mutane dubu 200 sun yi gangamin goyon bayan ɗan Basaraken Iran na ƙarshe

15.02.2026 08:22 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
China ta janye harajin shigar da kaya kan dukkan ƙasashen Afrika banda Eswatini China ta sanar da shirin janye haraji kan dukkanin kayakin da za a shigar mata daga ilahirin ƙasashen Afrika in banda Eswatini wadda ke ci gaba da ƙarfafa alaƙa da yankin Taiwan.

China ta janye harajin shigar da kaya kan dukkan ƙasashen Afrika banda Eswatini

15.02.2026 07:55 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Najeriya ta shiga sahun ƙasashen da ke da tarin ƙananan yara ɗauke da makamai Wasu alƙaluma da Majalisar ɗinkin duniya ta fitar sun nuna yadda Najeriya ta tsinci kanta a sahun ƙasashen da ke da yawan ƙananan yara masu riƙe da makamai don yiwa wani ɓangare yaƙi walau bisa tilasci ko bisa raɗin kai.

Najeriya ta shiga sahun ƙasashen da ke da tarin ƙananan yara ɗauke da makamai

15.02.2026 07:28 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
ƴanbindiga sun hallaka mutane da dama tare da kona gidaje a Neja Ƴanbindiga su kai hari kan wasu al’umomi a karamar hukumar Borgu ta jihar Neja a tsakiyar Najeriya inda suka hallaka mutane da dama tare da kwashe wasu da ba'a san adadinsu ba.

ƴanbindiga sun hallaka mutane da dama tare da kona gidaje a Neja

14.02.2026 20:27 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Ya zama dole a daina kashe Falasɗinawa - AU Shugaban Tarayya Afirka AU ,Ali Youssouf, ya bukaci kawo ƙarshen kisan kiyashin da ake yi wa Falasɗinawa.

Ya zama dole a daina kashe Falasɗinawa - AU

14.02.2026 17:59 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Kotu a Kamaru ta bukaci cigaba da tsare masu zanga-zanga su 148 a gidan yari Kotun soji a ƙasar Kamaru  ta ɗage shari’ar da ake yi wa  wasu mutane 148 bisa zargin yin tawaye da yaɗa labaran karya zuwa ranar 12 ga watan Maris mai zuwa.

Kotu a Kamaru ta bukaci cigaba da tsare masu zanga-zanga su 148 a gidan yari

14.02.2026 17:32 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Amurka ta aika ƙarin jiragen yaƙi gabas ta tsakiya gabanin tattaunawa da Iran Amurka ta sake aikewa da wani jirgin ruwan dakon jiragen yaƙi zuwa gabas ta tsakiya wanda ta taso daga gaɓar ruwan Caribbean lamarin da ke mayar da makamantan jiragen zuwa guda biyu da Washington ke da su a yankin dai dai lokacin da ake fargabar ɓarkewar yaƙi tsakaninta da Iran.

Amurka ta aika ƙarin jiragen yaƙi gabas ta tsakiya gabanin tattaunawa da Iran

14.02.2026 09:26 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Madagascar ta nemi tallafin ƙasashe bayan guguwa ta tagayyara jama'arta Madagascar ta yi shelar neman tallafin ƙasashen duniya bayan ta’azzarar ɓarnar da ƙaƙƙarfar guguwar Gezani da ta afka wa ƙasar ta yi, bayan da ta tagayyara ɗimbin al'umma tare da rusa tarin gine-gine a birnin Toamasina na biyu mafi girma a ƙasar ta nahiyar Afrika.

Madagascar ta nemi tallafin ƙasashe bayan guguwa ta tagayyara jama'arta

14.02.2026 09:12 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Kisan ɗimbin fararen hular da RSF ta yi a Sudan ka iya zama laifukan yaƙi- MDD Hukumar kare haƙƙin ɗan adam ta Majalisar ɗinkin duniya ta ce laifukan take haƙƙi da cin zarafin da mayaƙan RSF suka aikata a birnin al-Fashir na Sudan ka iya girmama zuwa matakin laifukan yaƙi.

Kisan ɗimbin fararen hular da RSF ta yi a Sudan ka iya zama laifukan yaƙi- MDD

14.02.2026 08:59 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Sojojin Najeriya sun kashe tarin ƴan ta’adda tare da ceto fararen hula 50 Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da kisan tarin ƴan ta’adda a hare-haren da ta ce sojojin ƙasar sun kai kan tarin maɓoyar ɓatagarin a sassa daban-daban na ƙasar cikin makon jiya wanda ya kai ga kamo ƴan ta’adda aƙalla 38 da kuma ceto mutane fiye da 50 da ke tsare a hannun ɓatagarin.

Sojojin Najeriya sun kashe tarin ƴan ta’adda tare da ceto fararen hula 50

14.02.2026 08:31 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
INEC ta sanar da ranakun da za a gudanar da manyan zaɓukan Najeriya Hukumar zaɓe a Najeriya INEC ta sanar da ranar 20 ga watan Fabarairun 2027 a matsayin ranar da za a gudanar da babban zaɓen ƙasar da ya ƙunshi na shugaban ƙasa da ƴan majalisun tarayya.

INEC ta sanar da ranakun da za a gudanar da manyan zaɓukan Najeriya

14.02.2026 08:18 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Babbar jam’iyyar adawar Bangladesh ta lashe zaɓen ƙasar da gagarumin rinjaye Hukumar zabe a Bangladesh ta ce babbar jam’iyyar adawar ƙasar BNP ta yi nasarar lashe zaɓen raba-gardama a juma’an nan da gagarumin rinjaye, karon farko tun bayan mumunan rikicin da ya afkawa ƙasar a shekarar 2024.

Babbar jam’iyyar adawar Bangladesh ta lashe zaɓen ƙasar da gagarumin rinjaye

13.02.2026 12:03 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Donald Trump ya kawo karshen shirin baƙin haure a jihar Minnesota Gwamnatin Shugaba Donald Trump ta sanar da kawo ƙarshen wani gagarumin aikin jami'an shige da fice kan baƙin haure a jihar Minnesota.

Donald Trump ya kawo karshen shirin baƙin haure a jihar Minnesota

13.02.2026 11:49 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0
Preview
Angola ta buƙaci sabuwar yarjejeniyar tsagaita a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo Gwamnatin Angola ta gabatar da wata sabuwar shawara ga dakarun dake fafatawa a gabashin Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo domin tsagaita wuta.

Angola ta buƙaci sabuwar yarjejeniyar tsagaita a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Congo

13.02.2026 11:36 — 👍 0    🔁 0    💬 0    📌 0

@ha.rfi.fr is following 6 prominent accounts